Masarautar Rano ta hukunta Hakimai da sukayi wa sarkin Kano Sunusi mubaya’a

by Dabo Online
0 comments

Masarautar Rano dake jihar Kano ta hukunta wasu hakimanta da suka bijerewa umarnin Sarki.

Hakiman garin Bebeji dana Tudun Wada ne suka karbi hukunci dakatarwa daga masarautar.

A cikin wata takada mai lamba REC/HD//1/VOL1/006 da REC/HD//1/VOL1/004 dauke da sa hannun sakataren masarautar Rano, Muhammad Idris Rano, tace ta dakatar da hakiman Bebeji da Tudun Wada kamar yadda Dabo FM ta tattaro.

Masarautar Rano tace sun bijirewa kira da Sarkin Rano, Alhaji Tafida Ila, yayi musu na zuwa gaisuwar Sallah tare da kawo dawaki da jama’arsu domin yin hawa salla a yankin na Rano.

Sai dai hakiman sun bijirewa umarnin inda suka kai gaisuwarsu ga Sarkin Kano, Muhammadu Sunusi II, tare da yin hawan sallar Idi da hawan Daushe da aka gudanar a jihar.

6F62E9E5 0988 413A 9182 3715D8B62E78 - Dabo FM
ZUwa ga Hakimin Tudun Wada
BD8A3578 8F69 4ADB 8F6D B0FBEDBC1AE1 - Dabo FM

Karin Labarai

You may also like

-
00:00
00:00
Update Required Flash plugin
-
00:00
00:00