0
Rundunar ‘yan kwamatin hadin gwiwa mai taken ‘Coalition Joint Task Force’ na reshen jihar Kaduna sun shiga chafke masu askin banza a cikin da wajen gari domin yi musu aski da almakashi a wani sumame da suka kira ‘Rabawa Gayu Goron Sallah’.
Dabo FM ta rawaito hadin gwiwar kungiyar ta fitar da hakan ne a yammacin Litinin 1 ga Sallah a shafinta na kafafen sadarwa, matasan dai an chafke su ne suna tsaka da bikin sallah a fadin jihar.
