Minista Sadiya Umar Faruq, ta nesanta kanta da wani rubutu da wani shafin Twitter ya fitar mai dauke da sunanta inda inda ya bayyana cewa “Babu maganar aurenta da shugaba Buhari.
Tin dai da safiyar yau ne shafin ya fitar da wani rubutu a matsayin Ministar inda aka bayyana cewa; “Nida da shugaba Buhari da Aisha Buhari, mun dade muna alakarmu mai kyau. Babu maganar aure tsakaninmu.”
“Labaran da ake ta yadawa, ba gaskiya bane.”
Ministar ta shafinta na ainahi @Sadiya_Farouq, ta karyata rubutun da wancen shafin ya rubuta, ta kuma nesanta kanta da mallakar shafin.
It has come to my attention that a fake Twitter account @Sadiya_farouq_ has been created in my name. I wish to inform my followers and well meaning Nigerians to disregard the handle and any information posted on it. My official Twitter handle remains @Sadiya_farouq Thank you