Gwamnatin jihar Kano ta kaddamar da aikin tituna da rijiyoyin burtsate a guraren da za a sake zabe

by Dangalan Muhammad Aliyu
0 comments

A daren jiya Juma’a 15/03/19, gwamnatin jihar Kano karkashin gwamna Dr Abdullahi Ganduje ta kaddamar da fara aikin titi a mazabar Gama dake karamar hukumar Nassarawa.

E90E2831 8A12 4463 9CC1 04E1664D69B4 - Dabo FM

Sabon Titin unguwar Gama, Brigade a karamar hukumar Nassarawa.

Al’ummar wannan yanki sun tashi da ganin manyan motocin tituna da kuma na haka rijiyar burtsate.

Bayan dan buncike da muka gudanar, mun gano cewa gwamnatin na da bukatar gina rijiyoyin burtsatsen sama da guda 40 a cikin mako guda.

31338586 493B 45B8 9736 CEE7705322CA - Dabo FM

Mazabar Gama na daya daga cikin mazabun da za’a sake gudanar da zaben gwamna a fadin jihar Kano, mazabar da tafi kowacce mazaba girman masu kada kuri’a a cikin jerin mazabun da za’a sake gudanar da zaben.

272F30E3 8C65 4DB2 B12F 218CE3DCE4BD - Dabo FM

Duk a sabon titina na Gama

Sai dai bisa dukkan alamu, al’umnar yankin dama masu amfani da shafukan sada zumunta musamman na Facebook, sun baiwa titin sunan ABBA GIDA GIDA ROAD.

Karin Labarai

You may also like

-
00:00
00:00
Update Required Flash plugin
-
00:00
00:00