Wasu Ɓata-Gari sun guntule hannun Matashi bayan sun Kwace masa Babur a Sokoto

by Dabo Online
0 comments

Habibu Abubakar, dalibi a jami’ar Usman Danfodio dake jihar Sokoto, ya hadu da iftila’i bayan da ‘yan daba suka guntule masa hannu tare da kwace masa babur dinshi na hawa.

Jaridar Daily Nigerian ta rawaito cewa, a daren jiya Lahadi, ‘a unguwar Maina, cikin gari, ‘yan daban suka guntule masa hannu tare da kwace babur din dalibin.

 

F60F423D 36D9 46C0 8548 16A28CA83248 - Dabo FM

Dalibi Habibu Abubakar

Mahaifin dalibin, Mallam Attahiru Abubakar ya tabbatarwa da jaridar faruwar al’amarin.

Yace

“Abin ya faru ne da misalin karfe 2 na daren Lahadi bayan sun dana masa tarko, inda suka kwace masa babur kuma suka guntule hannayenshi. Sun barshi jini yana ta malala.”

“Anyi kokarin sanar da Kawun Abubakar da hanzari, hakan tasa aka garzaya dashi asibiti dake Wammako cikin gaggawa domin ceton rai.”

C71546D2 E7D0 481E A124 5850957853DE - Dabo FM

Guntulallen hannun Habibu

Anyi kokarin jin ta bakin mai magana da yawun rundunar ‘yan sandan jihar ta Sokoto, amma hakar ta gaza cimma ruwa.

Karin Labarai

You may also like

-
00:00
00:00
Update Required Flash plugin
-
00:00
00:00