Gwamnatin Tarayya ta bawa masu Aski 20 ‘yan yankin Niger-Delta tallafin Naira Miliyan 88

by Dabo Online
0 comments

Gwamnatin Tarayya ta rabawa masu sana’ar aski guda 20 ‘yan asalin yankin Niger Delta Naira miliyan 88 a matsayin tallafi karkashin hukumar dake yiwa ‘yan yankin afuwa.

Ko wanne daga cikin wadanda suka amfana da shirin, zai samu Naira miliyan 4.4 a matsayin tallafin.

A takarda mai lamba PRO/SAP&CAP/TOVO/2019/0010/V/C.1009, wacce aka aike ranar 24 ga watan Janairun 2019 daga Gwamnati zuwa ga Manajan kwafanin TOVO VICKS NIGERIA ENT. LIMITED da zaiyi kwangilar bada tallafin.

E0ABA976 6CBB 4533 AE91 B2B95F506CEA - Dabo FM

Wannan ne karo na biyu da gwamnatin take bada tallafin ma’askan a yankin.

A wata takardar dai da gwamnatin karkashin ofishin afuwa ga ‘yan Niger Delta wacce aka aikewa kamfanin MESSERS TEMONGROVE LIMITED a ranar 5 ga watan Nuwanbar 2018.

Ta nuna cewa hukumar ta ware Naira Miliyan 90, domin rabawa ma’aska 20 kudin a matsayin tallafi.

CD829347 57C5 441E BAE2 66C379C3D34C - Dabo FM

Inda su kuma kowanne daga ciki zai amfana da Naira Miliyan 4.5.

Kudin tallafin ya kunshi, kudin hayar shago.

Karin Labarai

You may also like

-
00:00
00:00
Update Required Flash plugin
-
00:00
00:00