Zaben Kano: Takai bai ce a zabi Ganduje ba – Yasir Ramadan

by Dangalan Muhammad Aliyu
0 comments

Yasir Ramadan Gwale, dan gwagwarmaya kuma halastaccen mabiyin Mallam Salihu Sagir Takai, dan takarar gwamnan Kano a  jami’iyyar PRP, yace Takai bai umarci magoya bayanshi su marawa Ganduje baya ba.

“Ina so nayi kira ga jama’a da su yi watsi da duk wata sanarwa da Dawisu da yaransa suke yi akan Malam Salihu Sagjr Takai. Ba su da wata alaka da shi da zasu yi magana a madadinsa.”

“Malam Auwalu Muazu shi ne halastaccen mai magana da yawun Malam Salihu Sagir Takai kuma bai bayar da wannan sanarwa da su Dawisu suke yadawa ba.”

82446795 E6FE 43D7 ABFA 56A7D76D2D7E - Dabo FM

Daga shafin Ramadan Gwale

A safiyar yau ne mataimakin gwamnan Ganduje na fannin yada labarai, Salihu Tanko Yakasai ya fitar da sanarwa cewa Malam Salihu Sagir Takai ya umarci mabiyanshi da su zabi Dr Abdullahi Umar Ganduje na jami’iyyar APC.

9F57173C 3F17 42ED A0C0 A05D4810B128 - Dabo FM

 

Karin Labarai

You may also like

-
00:00
00:00
Update Required Flash plugin
-
00:00
00:00