Abdulaziz Yari ya mikawa Matawalle takardun mulkin jihar Zamfara

by Dabo Online
0 comments

Gwamnan jihar Zamfara mai barin gado, Gwamnan Abdulaziz Yari ya bawa Bello Muhammad Matawalle, zababben gwamnan jihar, takardun kama aiki a yau Laraba, 28/05/2019.

Ana sa ran rantsar da sabon gwamnan a gobe Alhamis, 29 ga watan Mayu, 2019 kamar yadda dokar Najeriya ta shirya.

Nasarar Matawalle da zo ne bayan da babbar Kotun koli ta ruguje ‘yan takarkarun jami’iyyar APC ciki hadda ‘dan takarar gwamnan jihar ta Zamfara.

C6F420B7 EC88 4C81 9E21 0F07B240C455 - Dabo FM

Hakan yasa jami’iyyar APC ta rasa dukkanin kujerar mulki a jihar Zamfara.

DaboFM ta tattaro cewa; jami’iyyar APC ta lashe dukkanin mukaman mulkin a jihar, kafin daga bisani kotu ta ruguje su bisa rashin gudanar da zaben fidda gwani a jami’iyyar.

C465B521 C408 45BC 84E3 A2B16DFB1C27 - Dabo FM

Karin Labarai

You may also like

-
00:00
00:00
Update Required Flash plugin
-
00:00
00:00