Tsohon gwamnan jihar Osun, Rauf Aregbesola ya yi doguwar addu’a a lokacin daya bayyana a gaban zauren Majalissar Dattijai domin tantanceshi kan zama Minista a Najeriya.
DABO FM ta binciko cewa Aregbesola yayi doguwa adddu’a ta addinin Islama kafin ya fara bayani a gaban majalissar data zaune a ranar 29 ga watan Yuli.
Kalli bidiyon;
Bidiyon NTA
An bayyana Aregbesola a matsayin mutum mai riko da addinin musulunci tare saka addini a duk lokacin da yake wani lamari.