Home LabaraiAn sace ɗaliban Islamiyya su 200 a jihar Neja

An sace ɗaliban Islamiyya su 200 a jihar Neja

by Dangalan Muhammad Aliyu
0 comments

‘Yan bandiga sun sace ɗaliban makarantar Islamiyya ta je ka ka dawo su 200 a garin Tegina da ke ƙaramar hukumar Rafi a jihar.

Wani mazaunin yankin, Zayyad Muhammad ya tabbatar wa Sahelian Times faruwar al’amarin.

Rahotanni su bayyana cewa ‘yan bindgar sun sace ɗaliban a makarantar Islamiya ta Saleh Tanko da misalin ƙarfe 4:30 na yammacin ranar Lahadi.

A yayin harin ta’addancin, an harbi mutum guda har lahira, dayan kuma yana can rai a hannun Allah.

Har kawo yanzu, rundunar yan sanda ba ta ce komai a kan faruwar al’amrin ba.

You may also like

-
00:00
00:00
Update Required Flash plugin
-
00:00
00:00