Home LabaraiKwabid19: Har yanzu akwai dokar zaman gida a Kano – Ganduje

Kwabid19: Har yanzu akwai dokar zaman gida a Kano – Ganduje

by Dabo Online
0 comments
Kwabid19 Ganduje

RAJASTHAN: Sanarwa da gwamnan jihar Kano, Dr Abdullahi Umar Ganduje, ya fitar ta hannun kwamishinan yada labarai, Muhammadu Garba ya fitar, yace har yanzu akwai dokar zaman gida a jihar Kano.

DABO FM ta tattara cewar gwamnatin tarayya ta sassauta dukkanin dokar zaman gida a fadin Najeriya tare da bai wa gwamnoni damar bada izinin bude Masallatai da Coci dake fadin Najeriya.

“Dokar hana zirga-zirga ta koma daga karfe 10 na dare zuwa 4 na asuba.”

A cikin sanarwa da gwamnatin Kano ta fitar, Gwamna Ganduje ya amince da bude dukkanin kasuwanni dake fadin jihar Kano. Sai dai fa gwamnan ya ce za a bude kasuwannin ne a iya ranakun da gwamnatin jihar ta amince a bude gari.

DABO FM ta tattara cewar ranakun da gamnatin Kano ta ware sun hada da Laraba, Juma’a da ranar Lahadi.

You may also like

-
00:00
00:00
Update Required Flash plugin
-
00:00
00:00