Home LabaraiGwamnatin Gabon ta tsayar da yunkurin juyin mulki, ta kama sojoji

Gwamnatin Gabon ta tsayar da yunkurin juyin mulki, ta kama sojoji

by Dabo Online
0 comments

Gwamnatin kasar Gabon tace ta samu tsayar da yinkurin da sojoji sukayi nayi mata juyin mulkin a safiyar Litinin.

An kama sojoji biyar da suka jagoranci kwace gudanarwar babban gidan rediyon kasar kamar yadda kakakin gwamnatin Guy Betrand ya shaida wa Radio France International.

An kafa dokar hana fita a Libreville babban birnin kasar.

A safiyar Litinin ne sojojin suka bada sanarwar kwace jan ragamar mulkin kasar da shugaba Ali Bango yake jagoranta tin shekarar 2009.

You may also like

-
00:00
00:00
Update Required Flash plugin
-
00:00
00:00