0
An kara samun mai dauke da cutar Kabid-19 ta haife jariri a jihar Legas.
Majiyar Dabo FM ta bayyana gwamnan jihar Legas, Babajide Sanwa-Olu ne ya sanar da hakan a kan shafinsa na Twitter.
Wannan na zuwa ne bayan kwana hudu da haihuwar wata mata mai cutar a asibitin Koyarwa na Idi-Araba.
Sai kuma rahoton da ya ishemu na mutum 3 sun rasu a jihar, rahoton da aka fitar ranar Juma’a, wanda ya hada jimillar mutane 36 ne suka rasa rayukan su.
Inda aka sallami mutum 67 kamar yadda rahoton Radio Nigeria ta bayyana a yammacin yau.
