Home LabaraiA gaggauce: ‘Bam’ ya tashi a Katsina

A gaggauce: ‘Bam’ ya tashi a Katsina

by Dabo Online
0 comments

An samu fashewar wani abu da ake tunanin Bam ‘IED Bomb’ ne  a kauyen Yammama dake karamar hukumar Malumfashi ta jihar Katsina.

Rahotanni sun ce abin fashewar ya tashi ne da safiyar Asabar a gonar wani mutum mai suna Alhaji Hussaini Mai Kwai, DABO FM ta tabbatar.

Kazalika Daily Trust ta rawaito cewar wasu shaidun gani da ido sun ce a kalla mutane 6 ne suka rasu sakamakon fashewar abubuwan.

“Na kirga gawarwaki 6 in da aka garzaya da wasu 5 zuwa asibiti. Jami’an tsaro suna kewaye da wajen a yanzu haka.”

Sai dai har zuwa yanzu, jami’an tsaro basu fitar da adadin wadanda suka rasu a sakamakon fashewar abubuwan ba.

Rundunar ‘yan sandan Najeriya reshen jihar Katsina ta tabbatar da faruwar al’amarin ta hannun mai magana da yawunta SP Gambo Isah.

You may also like

-
00:00
00:00
Update Required Flash plugin
-
00:00
00:00