An samu fashewar wani abu da ake tunanin Bam ‘IED Bomb’ ne a kauyen Yammama dake karamar hukumar Malumfashi ta jihar Katsina.
Rahotanni sun ce abin fashewar ya tashi ne da safiyar Asabar a gonar wani mutum mai suna Alhaji Hussaini Mai Kwai, DABO FM ta tabbatar.
Kazalika Daily Trust ta rawaito cewar wasu shaidun gani da ido sun ce a kalla mutane 6 ne suka rasu sakamakon fashewar abubuwan.
“Na kirga gawarwaki 6 in da aka garzaya da wasu 5 zuwa asibiti. Jami’an tsaro suna kewaye da wajen a yanzu haka.”
Sai dai har zuwa yanzu, jami’an tsaro basu fitar da adadin wadanda suka rasu a sakamakon fashewar abubuwan ba.
Rundunar ‘yan sandan Najeriya reshen jihar Katsina ta tabbatar da faruwar al’amarin ta hannun mai magana da yawunta SP Gambo Isah.
