Home LabaraiAn samu danyen Fetur a yankin Arewa maso Gabashin Najeriya – NNPC

An samu danyen Fetur a yankin Arewa maso Gabashin Najeriya – NNPC

by Dabo Online
0 comments

Hukumar NNPC ta ayyana samun danyen Man Fetur a yankin Arewa maso Gabashin Najeriya.

Manajan hukumar ta rikon kwarya, Samson Makoji, ne ya sanar da haka a cikin wata sanarwa daya fitar ranar Juma’a.

Hukumar dai ta sanar da gano danyen man ne a Kogin Kolmani na biyu dake Benue Upper Trough, Gongola Basin ta yankin Arewa maso Gabashin Najeriya.

Tin dai a watan Fabarairun 2019, shugaba Muhammadu Buhari, ya kaddamar da fara hakon duba man a yankin.

Mista Samson ya bayyana cewa; bayan doguwar haka da hukumar ta NNPC ta gudanar a tafkin, ranar Alhamis da misalin karfe 9:20 na dare, daya daga cikin durakun da aka ajiye domin tara ma’adanan da za’a hako, ta cika da Gas.

You may also like

-
00:00
00:00
Update Required Flash plugin
-
00:00
00:00