Gwamnan jihar Ribas, Nyesom Wike, yace Gwamnatin jihar bata rushe Masallaci kamar yacce ake ta yadawa ba.
Gwamnan ya bayyana labaran a matsayin na karya, ya kuma kalubalanci wadanda suke cewa an rusa Masallacin su fito su nuna inda aka rusa.
DABO FM ta tattaro cewa; Gwamnan yayi jawabin ne ta hannun mataimakin gwamnan a fannin kafafofin sadarwa, Simeon Nwakaudu, a yayin da ya ganawa da ‘yan Jarida a wajen da ake zargin gwamnatin da ruguza Masallacin.
Gwamnan yace masu yada labaran suna yi ne domin wata manufarsu ta daban wacce bata da kyau.
Ya kara da cewa; “Wasu manyan mutane a Najeriya suyi ta kirana a waya, suna fada min labarin karyar da yake ta yawo.”
“Yanzu dai gani da ku anan gurin, kunga babu wani masallaci anan.”
