Home WasanniMan City ta ragargaje Chelsea (6:0)

Man City ta ragargaje Chelsea (6:0)

by Dabo Online
0 comments

Kungiyar kwallon kafa ta Manchester city ta ragargaza takwarta ta Chelsea da ci shida da nema a yammacin yau Lahadi.

Wasan da aka buga a birnin Manchester, ya baiwa kungiyar ta Manchester City damar darewa kan teburin gasar Premier League ta kasar Ingila.

Dan wasa Raheem Sterling, shine ya fara jefawa Manchester City kwallo a minti na 4, yayinda Sergio Aguero ya jefa ta biyu a minti na 13.

Raheem Sterling (minti na 4, 80)

Sergio Aguero (Minti na 13 , 19, 16(P))

Ilkay Gundogan (Minti na 25)

Wannan ne karo na farko da mai horarwa na kungiyar ta Chelsea, Sarri yasha babban kayin da aka zura masa kwallo shida a raga.

Yanzu dai Chelsea ta koma mataki na shida, Manchester United kuma tana mataki na hudu.

You may also like

-
00:00
00:00
Update Required Flash plugin
-
00:00
00:00