1
Mai alfarma Sarkin Musulmi, Abubakar Saad III, ya sanar da ranar Talata, 23 ga watan Yuni a matsayin ranar 1 ga watan Dhul Hajji na shekarar 1441 bayan Hijira.
Cikin wata sanarwa mai dauke da sa hannun mai shugaban kwamitin harkokin addinin Musulunci , Farfesa Sambo Junaidu Wali ya fitar, ya ce Sarkin Musulmi ya amince da ranar Talata sakamakon rashin ganin wata da ba a yi ba a sassan Najeriya.
“Sarkin Musulmi ya amince da bayanan kwamitin ganin wata da na harkokin addinin Musulunci a fadarsa, don haka ya sanar da ranar Talata, 23 ga watan Yuni a matsayin ranar 1 ga watan Dhul Qadah.”
