Biyo bayan bayyana neman aure da tsohon shugaban Najeriya, Janar Babangida yace yanayi, mata dayawa sun nuna sha’awar auren IBB.
A wata tattaunawa da Janar Babangida yayi da jaridar Sun wacce aka wallafa a jiya Asabar, IBB ya sha’awarshi kan samun matar aure “kafin lokacin tsufa yazo” masa – Kamar yacce ya bayyana.
DABO FM ta tattaro tururuwar yan mata musamman na Arewa da suka nuna sha’awarsu akan auren tsohon shugaban kasa a kafafen sada zumunta.
Daga cikin mata akwai wadanda suka aike mana da sakonni a kan shafin mu na Facebook da wadanda suka bayyana sha’awar tasu a dandalinmu na muhawarar Facebook.
Kadan daga cikin sakonnin da muka samu akan ‘Facebook‘ da ‘Whatsapp‘
Wacce ta bukaci mu boye sunanta ta shaida cewa; “Ya samu, yazo zan aure shi. Ko an riga ni, Allah ya halartawa namiji auren Mata 4, to babu damuwa zan iya zama ta hudu. Wallahi ko a kwarkwara ba damuwa, ballantana ma yana kallo na zai “hola”.
Wata mai suna Maryam tace; “Ni babba ce yazo zan auresa”
Daga dandalinmu na Facebook kuwa, mun samu sakonni kamar haka;
Imanatu tace; “Gani abi ni lambarshi ko ayi mishi magana.“
Hadiza; “Gani, kuma shekaruna sun ja, inaga watakila ko yar shekara 59 tayi maka, amma ni ‘yar talakawa ce.”
Zahra; “Hh, aurenso nake so ba na kudi ba.”
Binta; “Ka nema da kanka.”
Sai dai a nashi bangaren, Janar Babangida ya bayyana cewa zan yi adalci wajen kin auren budurwa domin kada ya takura wa rayuwarta.
