Home LabaraiƘarya kawai Atiku yake shirgawa ‘yan Najeriya akan bashin da muke ci -Minista

Ƙarya kawai Atiku yake shirgawa ‘yan Najeriya akan bashin da muke ci -Minista

by Muhammad Isma’il Makama
0 comments

Tun da fari, tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya bayyana Najeriya na biyan bashin kaso 99 cikin dari na kudin shiga, inda yayi nuni da cewa a farkon shekarar nan Najeriya ta samu biliyan N950.56 inda kuma ta biya bashin biliyan N943.12.

Rahoton DABO FM ya bayyana Ministan yada labarai, Lai Mohamed ya yi martani kan kalaman Atiku da sanyin safiyar Laraba, na cewa tsohon mataimakin shugaban kasar karya kawai yake fadawa yan Najeriya.

Lai yace “Kalaman da Atiku keyi ba komai bane illa fatan Najeriya ta fada matsanancin hali, kuma har yanzu mun rasa gano inda ya samo alkaluman mun biya bashin biliyan N943.12 kana kuma mun sami kudin shiga biliyan N950.56 a farkon shekarar nan ba.”

Ya kara da cewa “Daya daga cikin abinda yasa kudin shiga keyin kasa shine dogaro da man fetir kawai da kasar keyi.”

Zuwa yanzu dai bashin da ake bin Najeriya ya kai Biliyan Dubu N27.4 kamar yadda aka bayyana a Disambar 2019.

You may also like

-
00:00
00:00
Update Required Flash plugin
-
00:00
00:00