Home LabaraiKansila da wasu shafaffu da mai sun siyarda Na’urar bada hasken Lantarki a jihar Kaduna

Kansila da wasu shafaffu da mai sun siyarda Na’urar bada hasken Lantarki a jihar Kaduna

by Dabo Online
0 comments

An zargi Kansilan mulki mai sanya ido na mazabar Gona ta karamar hukumar Sabon Gari, tsohon Shugaban Kungiyar Sufurin Motoci na Dadi Motor Park, Alh Sale Jakis d aUsman Sulaiman Sarki, bisa hada baki da wasu masu ruwa da tsaki wurin siyar da na’urar bada hasken wutan lantarki.

Na’urar da tsohuwar shugaban karamar hukumar, Hajiya Amina Sulaiman Kwari, ta baiwa yankin.

Wani jagoran Al’ummar yankin Malam Ahmad Usman Mai Biredi, ya bayyana hakan, sa’ilin zantawar sa da manema labarai a Zaria.

Ya ce; “Rana tsaka aka zo da wata rubutacciyar takarda cewar, Shugaban karamar Hukumar Sabon Gari, Injiniya Muhammad Usman, ya bada umarnin tafiya da na’urar bada hasken wutan lantarkin.

Sai dai ya tabbatar cewar; Bisa binciken da suka yi sun gano cewar babu gaskiya a wannan batun.

A cewar shi, bayanan da ke zuwa masu kawo yanzu, shi ne tuni aka siyar da wannan na’urar a wani wuri na daban.

Malam Usman Mai Biredi, ya nemi mazauna yankin su kwantar da hankulan su ganin suna daukan matakan da suka dace domin shawo kan matsalar.

Sai dai a martanin da ya fitar, shugaban karamar hukumar Sabon Garin, Injiniya Muhammad Usman, ta bakin mai bashi shawara akan harkokin siyasa, Alh Yusuf Mai Zinaru, ya karyata.

Inda ya bayyana cewa shugaban karamar hukumar na da masaniya akan daukar na’urar kadai.

Sai dai yayi nuni kan cewa shugaban bai san da zance siyarda na’urar ba.

Ya kara da cewa dai tuni karamar hukumar ta dakatar da kansilan da ake zarginshi da jagoranta siyar da na’urar tare bada tabbacin cigaba da bincike akan batun.

Ya kara da cewa, karamar hukumar na yin duk mai yiwuwa domin dai-daita al’amura da kuma gudanar da ayyukan raya kasa.

You may also like

-
00:00
00:00
Update Required Flash plugin
-
00:00
00:00