Home LabaraiBayan matsin lambar kafa hukumar Nishadi, Malaman Saudia sun fara halarta Kade-Kade da ‘Waken Disco’

Bayan matsin lambar kafa hukumar Nishadi, Malaman Saudia sun fara halarta Kade-Kade da ‘Waken Disco’

by Dabo Online
0 comments

Bidiyon maganar yana chan kasa.

Biyo bayan yunkuri da fafutukar karfafar harkokin Nishadi da yariman kasar Saudiyya, Muhammad Bn Salman, yake yi, Malamai a kasar sun fara nemo wa shirin yi wake-wake da kayan sauti zamani hujja a cikin Musulunci.

Daga cikin malamin dai yace; “Tin lokacin Manzon tsira, Annabi Muhammad SAW, ana yin waka tare da yin kida da kayan sauti na wancen lokacin.”

DABO FM ta rawaito daga cikin malaman, Sheikh Adil al-Kalbani, limamin wani masallaci a birnin Riyadh, ya kawo wani Hadisin ya yace; Uwar Muminai, Aisha Bn Abu Abkr (Allah ya kara yarda a gareta) tayi waka tare da wasu makotanta guda biyu.

Malamin ya bayyana haka ne a yayin wata tattaunawa da yayi da gidan Talabijin na SBC dake kasar ta Saudiyya.

Sheikh al-Kalbani, ya sake fadar wani hadisin da yace; Manzon Allah SAW, ya ga wata mata, ya tambayi Uwar Muminai, Aisha R.A, ko ta san matar?. Bayan da ta amsa cewa bata santa ba, sai Manzon Allah SAW yace; Wannan itace Qena, mawakiyar zamaninmu” har ma kuma ya tambayeta ko zata yi mata (Aisha RA) waka.

Shehin Malamin ya kara bayyana cewa; Manzon Allah SAW; ya halarci taron daurin aure inda matar (Qaina) ta rera waka tare da ganga.

Ya yi nuni da cewa Hadisan sun hada tarihin al’ada tare da samun asali a bangaren Musulunci.

Sai dai jamhurin Malaman kasar da ake wa lakabi da ‘Orthodox Muslim’, sun cigaba da bayyana haramcin kade-kade.

Za’a iya ganin tallar da DABO FM ba tada hurumi ko hannu a ciki.

You may also like

-
00:00
00:00
Update Required Flash plugin
-
00:00
00:00