1
Hukumar yaki da cin hanici da yi wa tattalin arzikin kasa ta’annati a Najeriya EFCC ta ce ta cafke wani mutum da yake sojan-gona a matsayin shugaban hukumar wato Ibrahim Magu.
Rahiton Dabo FM da BBC ta ta rawaito cewa Ofishin hukumar na garin Fatakwal ne ya cafke “Ibrahim Magu” a ranar Laraba, kamar yadda ta sanar a shafinta na Twitter.
“Yana amfani da sunan ne wajen zambatar jama’a tare da bata sunan wasu manyan jami’an hukumar raya yankin Niger Delta ta NNDC,” in ji EFCC.
