Home LabaraiGwamnatin tarayya ta rage kudin litar man fetur zuwa N130

Gwamnatin tarayya ta rage kudin litar man fetur zuwa N130

by Dabo Online
0 comments

Gwamnatin tarayya ta rage kudin man fetur daga N145 zuwa N130 kowacce lita daya.

Shugaba Muhammadu Buhari ya amince da ragin yayin gudanar da zaman Majalissar Zartawa wanda aka gudanar a yau Laraba.

Hakan na zuwa ne bayan da farashin gangar mai a kasuwar duniya ya fadi warwas wanda karyewar na da alaka da barkewar cutar Corona Virus.

You may also like

-
00:00
00:00
Update Required Flash plugin
-
00:00
00:00