Home LabaraiAttajirar Najeriya ta bawa Najeriya tallafin Naira biliyan 1, zata rabawa Zaurawa da Marayu N25,000

Attajirar Najeriya ta bawa Najeriya tallafin Naira biliyan 1, zata rabawa Zaurawa da Marayu N25,000

by Dabo Online
0 comments

Folorunsho Alakija, attajirar da babu kamarta a Najeriya zata rabawa Zawarawa da marayu masu rijista a Najeriya N25,000 kowannensu.

Hakan na zuwa ne kwana 1 kacal bayan da ta bawa gwamnatin Najeriya tallafin kudin yakar Coronavirus kimanin Naira biliyan 1.

DABO FM ta tattara cewar Miss Florunsho Alakija zata baiwa marayu da zaurawa kudin ne a karkashin gidauniyarta mai taken ‘The Rose of Sharon’

A wata sanarwa da attajirar ta fitar a shafinta na twitter ranar 30 ga watan Maris, tace attajirar tare da mijinta Mista Modupe Alakija a karkashun kamfaninsu na Famfa Oil sun alkauranta baiwa Najeriya tallafin biliyan 1 domin yaki da Coronavirus.

Haka zalika a yau 31 ga watan Maris, attajirar tace zata raba kudaden ne ga dukkanin Zaurawa da marayu a Najeriya da suke da rijista a fadin jihohin Najeriya 36 da tarayya Abuja.

You may also like

-
00:00
00:00
Update Required Flash plugin
-
00:00
00:00