Home LabaraiBuhari ya amince da daukar ma’aikata 774,000

Buhari ya amince da daukar ma’aikata 774,000

by Dabo Online
0 comments

Shugaba Muhammadu Buhari ya bayar da umarnin daukar ma’aikata 774,00 domin taimakawa wajen yaki da cutar Kwobid-19 a Najeriya.

Ministar Kudi, Zainab Ahmad ce ta bayyana haka yayin wata ganawa da manema labarai yau Litinin a birnin tarayyar Abuja akan matakan kariya da gwamnatin tarayya take dauka wajen kare kasar daga annobar Kwobid-19.

Ministar ta bayyana cewar za a dauki mutane 1000 a kowacce karamar hukuma dake fadin Najeriya guda 774.

Ta kara da cewa gwamnatin ta ware kimanin Naira biliyan 60 domin biyan alawus na ma’aikatan da za a dauka tare da tabbatar da ayyukan sun tafi yadda aka tsara.

Haka zalika tace gwamnatin ta ware Naira biliyan 500 a matsayin kudaden da za a kashe biyo bayan ballewar annobar, kamar yadda kamfanin dillancin Najeriya na NAN ya fitar.

“An ware biliyan 500 domin ingantawa da gyaran fannin lafiya.”

You may also like

-
00:00
00:00
Update Required Flash plugin
-
00:00
00:00