0
Dan Majalisar jiha dake wakiltar Nassrawa ta Tsakiya, Alhaji Sulaiman Adamu, ya rasu.
Kamfanin dillanin labaran Najeriya, NAN ya rawaito cewar abokin aikin mamacin Alhaji Muhammad Okpoku, dan majalissa mai wakiltar kananun hukumomin Udege da Loko ne ya sanar da mutuwar a yau Juma’a.
Mamacin ya rasu ne a asibitin tarayya dake garin Keffi bayan wata yar gajeriyar rashin lafiya.
