Kwamitin ganin wata a Najeriya, National Moonsighting Committee Nigeria, ya tabbatar da rashin samun cikakken rahotan ganin wata a fadin tarayyar Najeriya.
DABO FM ta tattara cewar kwamitin ya bayyana haka cikin wata sanarwa da ya fitar a shafin Twitter.
Hakan na zuwa ne bayan wasu rahotanni da wasu kafafen sada zumunta suka yada cewar an ga jinjirin wata a jihar Bauchi da jihar Yobe a arewacin Najeriya.
Kazalika kwamitin yace mai alfarma Sarkin Musulmi, Abubakar Saad III zai yi karin bayani nan da wani lokaci.
There was no positive sighting report of the Shawwal crescent in Nigeria, tomorrow is 30th Ramadan. An official statement from the Sultanate will be released shortly.
— National Moonsighting Committee Nigeria (@moonsightingng) May 22, 2020
