Home LabaraiBuhari zai je kasar Nijar taron ECOWAS

Buhari zai je kasar Nijar taron ECOWAS

by Dabo Online
0 comments
Buhari Travels

Shugaba Muhammad Buhari zai tafi zuwa birnin Naimey na Jamhuriyar Nijar domin halartar taron kungiyar kasashen yammacin Afrika a ranar Litinin.

Ana tsammanin jin yadda yankin yake kokari kan yaki da cutar Koronabairas.

BAbban mataimakin shugaban a fannin yada labarai, Mallam Garba Shehu ne ya sanar da hakan a yau Lahadi.

DABO FM ta tattara cewar cikin sanarwar da Garba Shehu ya fitar, ya bayyana cewa shugaba Buhari zai halarci taron shuwagabannin kasashen kungiyar ECOWAS, taro na 57 da kungiyar ta gabatar.

Buhari zai bar Najeriya a gobe Litinin domin halartar taron.

You may also like

-
00:00
00:00
Update Required Flash plugin
-
00:00
00:00