Gadar kasan da gwamnati jihar Kano takeyi karkashin jagorancin Gwamna Dr Abdullahi Umar Ganduje a birnin Kano.
Gadar da take a titin Magaji Dambatta Road, tsohon shatale-talen Dangi.
Gwamnatin tace dai za’a kammala gadar cikin rabi zuwa karshen wannan shekarar da muke ciki ta 2019.
A cigaba da bunkasa hanya da gwamnatin keyi, Gwamnatin na kokari wajen kammala aiyukan tituna da gada wacce ta gada.
Sai dai a iya cewa gwamnatin jihar Kano tayi watsi da harkar Ilimi jihar, wanda yanzu a iya cewa yayi tabarbarewar da dukkan gwamnatoci da akayi a baya sunfi ta Mai girma Ganduje tabuka aiki a fannin Ilimi.