Folorunsho Alakija, attajirar da babu kamarta a Najeriya zata rabawa Zawarawa da marayu masu rijista a Najeriya N25,000 kowannensu.
Hakan na zuwa ne kwana 1 kacal bayan da ta bawa gwamnatin Najeriya tallafin kudin yakar Coronavirus kimanin Naira biliyan 1.
DABO FM ta tattara cewar Miss Florunsho Alakija zata baiwa marayu da zaurawa kudin ne a karkashin gidauniyarta mai taken ‘The Rose of Sharon’
A wata sanarwa da attajirar ta fitar a shafinta na twitter ranar 30 ga watan Maris, tace attajirar tare da mijinta Mista Modupe Alakija a karkashun kamfaninsu na Famfa Oil sun alkauranta baiwa Najeriya tallafin biliyan 1 domin yaki da Coronavirus.
Mr. and Mrs. Modupe and Folorunso Alakija through @FamfaOilLimited Pledge N1 Billion Naira to Support Nigeria’s Fight Against COVID-19 pic.twitter.com/hX543dkeoS
— Folorunso Alakija (@alakijaofficial) March 30, 2020
Haka zalika a yau 31 ga watan Maris, attajirar tace zata raba kudaden ne ga dukkanin Zaurawa da marayu a Najeriya da suke da rijista a fadin jihohin Najeriya 36 da tarayya Abuja.
