Home LabaraiBuhari ya naɗa sabbin hafsoshin tsaron Najeriya

Buhari ya naɗa sabbin hafsoshin tsaron Najeriya

by Dabo Online
0 comments

Shugaba Muhammadu Buhari na Najeriya ya naɗa sabbin shugabannin hafsoshin tsaron Najeriya bayan ya amince da saukar tsofaffin.

Sabbin hafsoshin su ne;

Major-General Leo Irabor, a matsayin sabon Shugaban ma’aikatan tsaro.

Major-General I. Attahiru, a matsayin sabon Babban hafson Sojan Ƙ asa.

Rear Admiral A.Z Gambo,  a matsayin sabon babban Hafson Sojan Ruwa.

Air-Vice Marshal I.O Amao, a matsayin sabon babban Hafson Sojan Sama.

Hakan na zuwa ne bayan shugaba Buhari ya amince da ajiye aikin tsoffin hafsoshin tsaron Najeriya da su ka dade suna riƙe da muƙaman.

You may also like

-
00:00
00:00
Update Required Flash plugin
-
00:00
00:00