Ministan sufuri na Najeriya Mr. Rotimi Amaechi ya bayyana cewar wasu marasa tarbiyya sun Kai masa hari a lokacin da ya halarci taro a birnin Madrid na kasar Andalus (Spain).
A cewarsa, ta shafinsa na Twitter, ya bayyana cewa wasu bata garin ‘yan Najeriya marasa tarbiyya sun kai masa hari yayin gudanar da taron chanjin yanayi a birnin Madrid na kasar Andalus.
Some minutes ago, I was attacked by a few misguided Nigerians while on national assignment at a climate change event in Madrid, Spain. They were quickly repelled by the Spanish police before they could do any harm. I am fine. I was not hurt. Thanks for your support & prayers.
Ministan yace cikin gaggawa jami’an ‘yan sanda sun yi kokarin tarwatsasu.
Ya kuma bayyana cewa yana yan cikin koshin lafiya, akan haka ya kara yin godiya a bisa addu’ar da ake yi masa ta masoya.
Taron dai da majalissar dinkin duniya ta shirya a wannan shekara ta 2019, wanda ake wa taken COP25, shine taro na ashirin da biyar da yake tattaunawa akan sauyin yanayi da dumamarsa a duniya.