Ganduje ya soke yin ‘Hawan Nassarawa’ da masarautar Kano takeyi duk ranar 3 ga Sallah

by Dabo Online
0 comments

Gwamnan jihar Kano, Dr Abdullahi Umar Ganduje ya soke gudanar da bikin hawan Nassarawa da masarautar Kano ta sabayi dukkanin kwanaki 3 bayan kowanne bikin Sallah.

DaboFM ta rawaito mai yada labaran gwamnatin jihar, Anwar , yace gwamna GAnduje ya soke yin hawan ne bisa wasu dalilan tsaro.

“Bayan ganawa da Ganduje yayi da jami’an tsaro kamar yadda aka sabayi a duk shekarar, an samu rahoto cewa akwai matsala daka iya kawowa zaman lafiya cikas.”

47DB6BED CF13 4518 BD78 0FA2E2752596 - Dabo FM

“Saboda dalilin rahotan da aka samu yayin ganawa da jami’an tsaro, gwamnatin jihar Kano ta soke hawan Nassarawa da masarautar Kano zatayi ranar 3 ga Sallah.”

“Tini dai gwamnatin jihar Kano ta sanar da masarautar Kano, bisa matsayarta na dakatar da hawan a cikin gari.”

Karin Labarai

You may also like

-
00:00
00:00
Update Required Flash plugin
-
00:00
00:00