0

Gwamnan jihar Kano, Dr Abdullahi Ganduje, ya tsige mai martaba Sarki Muhammadu Sunusi II.
Hakan na kunshe a jikin wata sanarwa da sakataren gwamnatin jihar Kano, Alhaji Usman Alhaji ya fitar a yau Litinin.
Sanarwar tace majalissar zartarwar jihar Kano ce ta amince da tube rawanin Sarki bisa samunshi da laifuka da suka hada da rashin biyayya.

