Ministan Ilimin Najeriya, Malam Adamu Adamu, yace za’a kashe kimanin naira biliyan 50 wajen karasa ginin babban dakin karatu dake garin Abuja.
Ministan yace gwamnatin shugaba Buhari zata bazatayi kasa a gwiwa ba wajen karasa duk wani aikin da ta gada daga gwamnatocin da suka shude.
A shekara 2006 aka fara kaddamar da shirin ginin akan kudi naira biliyan 8, a shekarar 2013 aka kara cire naira biliyan 18 wajen farfado da aikin. a cewar malam Adamu Adamu.
An kiyasta kashe naira biliyan 78 kafin daga bisani kudin ya zama biliyan 50 bayan sake duban kudin.