Uwargidan gwamnan jihar Kano, Dakta Hafsat Umar Ganduje, ta samu lambar yabo hadi da girmamawa daga Jami’ar BUK dake jihar Kano.
Kungiyar dake kula da tsari da gudanarwar Ilimi a Najeriya reshen Jami’ar ne ya baiwa Dr Hafsat Ganduje, lambar yabon ta hannun shugaban Shugaban Jami’ar Bayero, Farfesa Muhammad Yahuza Bello, a ranar Laraba.