0
Majalissar Dokoki ta jihar Bauchi ta tantance kwamishinoni 20 cif, kamar yadda Gwamnan jihar Alh. Bala Muhammad ya aike mata, a watan da ya gabata.
Kakakin majalissar dokoki ta jihar, Rtd. Hon. Abubakar Y Sulaiman ne ya jagoranci tantancewar a zauren majalissar dake birnin Yakubu.
Kwamishinonin dai guda 20 ne, kamar yadda Gwamnan ya tura da sunayen su a watan da ya gabata.
Hakan ya bayyana cewa kowacce karamar hukuma a jihar ta samu Kwamishina.
Tun a ranar Talata 3 ga watan Satumba ne majalissar ta fara zaman tantancen kwamishinonin, a jiya Laraba kuma ta kammala tamtance su baki daya.
