Home LabaraiMawakiya Maryam A. Baba ‘Sangandale’ ta kwanta matsananciyar rashin lafiya

Mawakiya Maryam A. Baba ‘Sangandale’ ta kwanta matsananciyar rashin lafiya

by Dabo Online
0 comments

An kwantar da fitacciyar mawakiyar Hausa, Maryam A Baba da aka fi sani da ‘Sangandale’ a asibiti sakamakon matsananciyar rashin lafiya.

Da yake fitar da labarin, abokin sana’arta, jarumi Abba El-Mustapha, ya bayyana cewar; Likitoci sun samu nasarar yi mata tiyata.

Sai dai bai bayyana ciwon da yake damunta.

Kazalika da take tabbatar da labarin, kanwar mawakiyar, Zainab A Baba, ta ce mawakiyar tana samun sauki bayan an kammala yi mata tiyatar.

You may also like

-
00:00
00:00
Update Required Flash plugin
-
00:00
00:00