Wasu fusatattun matasa masu zanga-zanga sun dira kantin Shoprite dake babban titin Lekki-Epe expressway a jihar Legas a ranar Talata, 3 ga Satumba, 2019.
Wannan abu ya biyo bayan hare-haren da aka kaiwa yan Najeriya da wasu kasashe a kasar Afrika ta kudu inda aka kona musu shaguna da wuraren sana’arsu.
Matasan sun kai wannan hari ne domin ramuwar gayya saboda kantin Shoprite na yan kasar Afrika ta kudu ne. Jami’an yan sanda sun shawo kan lamarin yanzu.