Home LabaraiTukunna: Atiku bai shiga hannun mu ba kan badakalar biliyan 75.3 -EFCC

Tukunna: Atiku bai shiga hannun mu ba kan badakalar biliyan 75.3 -EFCC

by Muhammad Isma’il Makama
0 comments

Hukumar yaki da cin hanci da rashawa, Efcc ta bayyana labarin dake yawo a kafafen sadarwa kan batun ta damke tsohon mataimakin shugaban kasa kuma dan takarar jamiyyar PDP a zaben shugabancin kasa daya gabata, Atiku Abubakar a matsayin labarin kanzon kurege.

Rahoton Dabo FM ya bayyana labarin dai ya yadu kan cewa hukumar ta tsare Atiku tare da maka shi gaban Majistire Mojisola Dada ta kotun kebattattun laifuka dake Ikeja, Lagos.

Mai rikon shugaban yada labarai na Efcc, Tony Orilade shine ya bayyana hakan, ya kuma ce babu wannan magana ta tsare Atiku kan badakalar biliyan 75.3. Kamar yadda DailyNigerian ta wallafa.

You may also like

-
00:00
00:00
Update Required Flash plugin
-
00:00
00:00