1
Gwamnan Kano, Dr Abdullahi Umar Ganduje , ya sanya dokar hana fita a jihar Kano baki daya.
Gwamnan ya bayyana haka ne yau Talata a fadar gwamnatin jihar.
DABO FM ta tattara cewar Ganduje yace dokar zata fara aiki ne daga ranar Alhamis 16 ga watan Afrilu da misalin karfe 10, za kuma ta kasance mai wa’adin mako guda.
Haka zalika, ma’aikatar lafiya ta jihar Kano, ta tabbatar da samun karuwa wadanda suka kamu da cutar Kwabid-19 a jihar.
Ma’aikatar da bayyana haka ne a ingantaccen shafinta na Twitter a yau Talata.
“A daidai karfe 6:00 na yammacin yau 14 ga watan Afrilu, an tabbatar da samun karin mai dauke da Coronavirus.”
