Home LabaraiYanzu-yanzu: An kara tsawaita dokar kulle a Kano na tsawon sati 2

Yanzu-yanzu: An kara tsawaita dokar kulle a Kano na tsawon sati 2

by Dabo Online
0 comments

Kwamitin yaki da cutar Koronabairas na kasa, ya kara tsawaita dokar kulle a jihar Kano ta tsawon mako 2.

Shugaban kwamitin, Boss Mustapha ne ya sanar da haka a yau Litinin yayin bayanai game da cutar Kwabid19 da kwamitin ya saba yi kullin a birnin Abuja.

DABO FM ta tattara cewar tin dai ranar 16 ga watan Afrilu, gwamnan Kano, Dr Ganduje ya fara sanya dokar hana fita a jihar na tsawon mako guda.

Bayan fargaba da karuwar masu dauke da cutar Kwabid19 suka yawaita a Kano, ranar 27 ga watan Afrilu, shugaba Buhari ya sanya sabuwar dokar zaman gidan na tsawon makonni biyu domin bai wa ma’aikatan lafiya damar bincike.

A bisa kiduddugar 17 ga watan Mayu, mutane 825 ne suka kamu da cutar a jihar Kano tare da samun mutuwar mutum 36.

Haka zalika mutum an sallami mutum 112, kamar yadda ma’aikatar lafiya ta jihar Kano.

Cikakken bayanin na zuwa…

You may also like

-
00:00
00:00
Update Required Flash plugin
-
00:00
00:00