0
Allah ya yi wa babban malamin addinin Islama, Sheikh Fadilu Dan Almajiri Fagge rasuwa yau Talata.
Kafin rasuwarshi, ya kasance shugaban limaman Juma’a na jihar Kano.
Malamin ya rasu ne a mahaifarshi ta Fagge, kamar yadda ‘yan uwanshi suka bayyanawa DABO FM.
A yanzu da karfe 9:30 na safe da muke hada wannan rahotan, mun samar sanarwar cewa za’ayi jana’izarshi a unguwar Fagge da karfe 1 na ranar yau kamar yadda addinin Musulunci ya tanada.
