Home LabaraiGanduje ya amince a bude dukkan kasuwannin Kano ranakun bude gari

Ganduje ya amince a bude dukkan kasuwannin Kano ranakun bude gari

by Dabo Online
0 comments
Kwabid19 Ganduje

RAJASTHAN: Gwamnan jihar Kano, Dr Abdullahi Umar Ganduje ya amince da bude dukkanin kasuwannin jihar Kano.

Sai dai gwamnan ya ce za a bude kasuwannin ne a iya ranakun da gwamnatin jihar take daga dokar zaman gidan da ta sanya. Ranakun da suka hada da Laraba, Juma’a da kuma Lahadi daga karfe 6 na safe zua 6 na yamma.

Babban mataimakin gwamnan a fannin yada labarai, Salihu Tanko Yakasai ne ya sanar da haka yau Litinin cikin wani sako da ya wallafa a shafukanshi na sada zumunta.

DABO FM ta ttara cewar a yau Litinin ne gwamnatin tarayya ta sassauta dokar zaman gida da ta sanya a fadin jihohin Najeriya, in da ta bayyana dokar zaman gida ta koma daga karfe 10 na dare zuwa 4 na Asuba.

Kazalika ta baiwa gwamnonin jihohin Najeriya damar bude masallatai da coci-coci dake fadin jihohinsu.

Kalli yadda aka fafata tsakanin sojoji da ‘yan sanda a Zaria.

You may also like

-
00:00
00:00
Update Required Flash plugin
-
00:00
00:00