Jarumin Kannywood Ali Nuhu ya na shan rubdugu daga matasan arewacin Najeriya a shafin sada zumuntar nan na Twitter.
Hakan na zuwa ne sakamakon furucin da jarumin ya yi kan rashin shigarshi zanga-zangar #EndInsecurityNow da aka shirya a Arewa domin ceto yankin daga matsalar rashin tsaro.
DABO FM ta tattara cewa; A wata hira da Ali Nuhu ya yi da sashin Hausa na rediyon DW, Ali Nuhu ya ce sukar da ya ke sha daga wajen ‘yan Twitter ce ta sanyashi bai shiga zanga-zangar ba.
“Wani lokacin sai kaga kamar ma kai a matsayinka na Tauraro in za ka shiga maganar kamar shisshigi za ka yi wa mutane, kaje Twitter, a nan ne za ka ga an sa taurarin Arewa, a zage su a kushe shu ayi musu wulakanci yadda rai yake so. Haka zalika a Facebook da Instgram.
Wannan shi ne dalilin mutane suke ja ba ya ba wai don ba sa son shigowa bane.”
Sai dai furucin jarumin ya kara hasala masu amfani da shafin Twitter wajen yi masa raddi da wasu suke ganin an yi masa ‘kaca-kaca.’
Ga wasu daga cikin irin martanin da aka yi wa jarumin.
I knew Ali Nuhu was finished when he became Ahmad Musa’s errand boy
Never rated him since then
— Sarki. (@Waspapping_) October 17, 2020
Ali Nuhu is a poor leader with zero sympathy of the brutalities in this Country. He's a disgrace for what he said. #SecureNorth #EndInsecurity
— Comrade ➐ (@Famous_Anfield) October 17, 2020
Ali Nuhu can’t speak about the killings happening in the north because some people are abusing them on social media but he can tell you who to VOTE during election period because he is getting paid for that. This shows He value money more than the lives of his people#SecureNorth
— Al'ameen✨ (@Al_ameen_Yabo) October 17, 2020
