Home NajeriyaShekaru hudun gaba zasufi tsanani – Buhari

Shekaru hudun gaba zasufi tsanani – Buhari

by Dangalan Muhammad Aliyu
0 comments

Zababben shugaban kasar Najeriya, Muhammadu Buhari yace zangon mulkinshi na biyu zai fi tsanani.

Shugaba Buhari yayi wannan furuci jiya, a wata ganawa da yayi da mukarraban gwamnatinshi a fadar Vill dake babban birnin tarayyar Abuja.

“Kar mutane su manta abinda na fada musu a wajen yakin neman zabe, akan habaka tattalin arziki, samar da aikin yi, tsaro da kuma cin hanci da rashawa, shekarar hudun da zamu shiga zatafi tsanani tare da tsaurarawa.”

A ranar Larabar data gabata ne dai hukumar zabe ta INEC ta bada tabbacin lashe zaben shugaba Muhammadu Buhari bayan da ya samu gagarumar nasara akan jami’iyyar hamayya ta PDP.

You may also like

-
00:00
00:00
Update Required Flash plugin
-
00:00
00:00