Home LabaraiA gaggauce: Ba za a yi jarrabawar WAEC ta bana ba – Gwamnati ta tabbatar

A gaggauce: Ba za a yi jarrabawar WAEC ta bana ba – Gwamnati ta tabbatar

by Dabo Online
0 comments

Gwamnatin tarayyar Najeriya ta tabbatar da cewar daliban ajin karshe da zasu kammala karatun Sakandire a bana, ba za su rubuta jarrabawar WAEC ba sakamakon cutar Kwabid-19.

Gwamnatin ta tabbatar da haka ne a zaman majalissar zartarwa na yau Laraba a fadar shugaban kasa ta Aso Villa.

Hakan na zuwa ne kwanaki kadan bayan da Karamin Ministan Ilimi, Chukwuemeka Nwajiuba ya bayar da sanarwar cewa za a yi jarrabawar a Najeriya.

Babban Ministan Ilimi, Adamu Adamu, da yake karin haske dangane da batun fasa yin jarrabawar a Najeriya, ya ce babu ranar bude makarantu a Najeriya har sai masana lafiya sun bayar da shaidar cewa al’amuran cutar Kwabid-19 sun daidaita.

Hukumar WAEC dai ta fitar da ranar 15 ga watan Agusta a matsayin ranar da za a fara jarrabawar a kasashen Afrika ta yamma.

Cikakken bayani yana zuwa.

You may also like

-
00:00
00:00
Update Required Flash plugin
-
00:00
00:00