Wasu masu dauke da makamai sun hallaka malamin addinin Kirista a cigaba da rikicin kabilu a jihar Taraba.
Limamin da aka bayyana da Rabaren David Tanko a Kufai Adamu, dan karamar hukumar Wukari, yana kan hanyarshi ta m zuwa garin Takum domin shirin sulhu akan rikicin da kullin yake kara tsamari tsakanin kabilun Tivi da Jukun.
Sashin Hausa na Legit.ng ya rawaito cewa; shugaban kwamitin zaman lafiya, Shiban Tikari ne ya sanar da hakan.
Ya kara da cewa; bayan sun kashe malamin, sai suka bankawa motarshi da gawarshi wuta.
Rahotannin sun bayyana cewa; ana zargin ‘yan kabilar Tibi da aikata kisan.
Bayan tuntuba don jin ta bakin rundunar ‘yan sandan jihar da Jaridar tayi, hakanta ya gaza cimma ruwa.
