Home LabaraiAn samu sabon ‘Dan Autan’ mawakan hip hop na Hausa bayan rasuwar ‘Lil Ameer’

An samu sabon ‘Dan Autan’ mawakan hip hop na Hausa bayan rasuwar ‘Lil Ameer’

by Dangalan Muhammad Aliyu
0 comments

Fitaccen mawakin Hausa Hip-hop, Amir Hassan dan asalin jihar Kano da ake yi wa lakabi da dan autan mawakan arewa da Allah ya yi wa rasuwa a shekarar 2017 ya samu magaji.

A lokacin da yaron mawakin ya rasu yana da shekara 14 a duniya, ya kuma rasu sakamakon hatsarin mota.

Sai dai bayan shekaru 3, an sake samun wani sabon yaron mawaki mai suna Abdullahi Mansur da ake yi wa lakabi da Oga_Abdul, dan asalin jihar Jigawa.

Sashin Matasa na DABO FM ta bincika cewar tini dai fitaccen jarumin Hausa, Adam A. Zango ya ayyana daukar matashin zuwa kamfaninshi na White House Family.

A zantawar DABO FM ta matashin, ya bayyana mana cewar yana karatu a Jami’ar Kimiyya da fasaha ta jihar Kano inda a yanzu haka shekara ta 3.

“Suna na Abdullahi Mansur wanda aka fi sani da Oga Abdul, ni haifaffen garin Gujungu ne daga jihar Jigawa. Na yi Firamare a Model Boarding Primary School RIngim, na yi Sakandire a GSTC Karkarna.”

“Yanzu haka ina KUST WUDIL shekara ta 3, ina karantar Biology. Shekarata 19 a duniya.”

Daga cikin wakokinshi akwai Mallam Bahaushe wadda zaku iya kalla a kasa.

 

View this post on Instagram

 

A post shared by j_boss (@iam_oga_abdul) on

Lil Ameer, wanda ake yi wa lakabi da dan autan mawakan hip hop na Hausa ya rasu.

Mawakin, wanda ya yi fice a jihar Kano da wasu yankunan arewacin Najeriya, ya rasu ne sakamakon hatsarin mota yana da shekara 14 a duniya.

You may also like

-
00:00
00:00
Update Required Flash plugin
-
00:00
00:00